in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaron MDD ya yi suka a kan mummunan harin da aka kai a kan iyaka tsakanin Sudan da Sudan ta kudu
2015-11-28 16:23:30 cri
Kwamitin tsaron MDD a ranar Jumma'an nan ya yi kakkausar suka game da harin da wadansu da ba'a san ko su wane ne ba suka kai a gidan basaraken garin Abyei , wanda ke kan iyakan kasashen Sudan da Sudan ta kudu, harin da ya hallaka wani ma'aikacin wanzar da zaman lafiya dan asalin kasar Habasha da kuma wata karamar yarinya.

Mambobin kwamitin sulhun a cikin sanarwar da suka fitar sun yi suka da kakkausar murya a kan duk hare-haren da neman tashin hankali da ake yi a yankin na Abyei dake karkashin sa idon wucin gadi na sojojin MDD wato UNISFA da wasu masu dauke da makamai ke yi.

Kwamitin mai mambobi 15 daga nan sai suka bukaci gwamnatocin kasashen biyu da cikin gaggawa su binciki wannan harin tare da neman taimako daga sojojin UNISFA inda suka jaddada cewa ya kamata a kame duk masu hannu a cikin wannan danyen aikin don su fuskanci hukunci.

Tun da farko dai a ranar Jumma'an, babban magatakardar MDD Ban Ki-Moon ya yi suka da kakkausar murya a kan harin da aka kai gidan babban basaraken Abyei, Ngok Dinka. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China