in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ta da boma-bomai a wani yankin birnin Kabul, inda gidajen jakadancin kasashen waje suke
2015-12-12 13:47:05 cri
Da maraicen ranar Jumma'a nan, 11 ga wata, wasu boma-bomai suka tashi a wani yankin birnin Kabul, inda gidajen jakadancin kasashen waje da dama suke, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane 4, tare da wasu 7 suka jikkata.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, wassu 'yan ta'adda biyar ne suka kai hari kan wani otel inda sojojin kasar Amurka su kan yi masauki, wanda kuma ke kusa da ofishin jakadancin kasar Spaniya dake ta kasar Afghanistan. Haka kuma wassu masu dauke da makamai guda biyu sun kutsa cikin ofishin jakadancin kasar Spaniya, amma an harbe su biyu duka.

A wurin da aka samu fashewar, Mr. Mariano Rajoy, mataimakin ministan kula da harkokin cikin gidan kasar Afghanistan ya gaya wa manema labaru cewa, wannan hari ne na kunar bakin wake da wata kungiyar 'yan ta'adda ta shirya. Tuni dai kungiyar Taliban ta sanar da daukar alhakin kai wannan hari. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China