in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira ga kasa da kasa da su yi kokarin shimfida zaman lafiya tare da sake gina kasar Afghanistan
2015-10-08 13:58:00 cri
A jiya ne zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD a birnin Geneva da sauran hukumomin kasa da kasa a kasar Switzerland Wu Hailong ya yi kira ga kasa da kasa da su yi kokarin shimfida zaman lafiya da sake gina kasar Afghanistan.

Mr Wu ya yi wannan kiran ne yayin da ya ke jawabi a taron kolin hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD karo na 66 kan batun 'yan gudun hijirar kasar Afghanistan.

Wu Hailong ya bayyana cewa, a sakamakon yake-yake da rikice-rikice, kasar Afghanistan ta kasance daya daga cikin manyan kasashen da suka fi fama da matsalar 'yan gudun hijira a duniya. Batun 'yan gudun hijira na kasar Afghanistan yana da nasaba da yunkurin sake gina kasar, kana ya yi babban tasiri ga kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar har ma a yankin baki daya.

Muddin ana bukatar warware matsalar 'yan gudun hijira a kasar, wajibi ne a yi kokarin shimfida zaman lafiya da sake gina kasar da kuma samun bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'umma a kasar.

Wu ya kara da cewa, kasar Sin tana fatan ganin an kara zuba jari da kara yin hadin gwiwa da kuma samar da sharadi don warware matsalar 'yan gudun hijira a kasar Afghanistan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China