in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta fitar da ra'ayinta na daidaita batun Sham a siyasance bisa matakai hudu
2015-10-31 13:21:51 cri
A ranar Jumma'a 30 ga wata, Mr. Li Baodong, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin a jawabin da ya gabatar a yayin taron ministocin harkokin wajen kasashe da aka yi kan batun Sham a Vienna, ya bayyana cewa, ya kamata a daidaita da kuma ci gaban matakan yakar ta'addanci da sassauta halin jin kai da ake ciki, da kuma yin shawarwarin siyasa a lokacin da ake kokarin daidaita rikicin kasar Sham.

Mr. Li har ila yau ya gabatar da ra'ayin gwamnatin kasar Sin game da daidaita batun Sham a siyasance bisa matakai hudu, wato da farko dai, ya kamata bangarorin da abin ya shafa su tsagaita bude wuta da kawo karshen nuna karfin tuwo, kuma su yi alkawarin tinkarar ta'addanci. Na biyu, ya ce bisa shugabancin MDD, bangarori daban daban na Sham su amince da juna, kuma su yi shawarwari daga dukkan fannoni cikin adalci don su fitar da jadawalin daidaita harkokin siyasa ta wucin gadi bisa sanarwar Geneva. Babban jami'in na kasar Sin ya kara da cewa, ya kamata a kaddamar da aikin sake bunkasa kasar Sham bayan yaki, ta yadda bangarori daban daban na Sham za su iya ganin makomar zaman lafiya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China