in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Senegal ta yi zabi kan noma domin rage rashin aikin yin matasa da barin kasarsu
2015-11-17 10:26:09 cri
Kwararru sun maida hankali a birnin Dakar a bangaren noma domin kafa ayyukan yi a kasar Senegal, da rike matasa a yankunansu daban daban, da yaki da yin hijira ba bisa doka ba.

An sanya wannan mataki a sahun gaba a yayin wani zaman taro da ya tattara wakilai 120 daga bangaren gwamnatin Senegal, masu zaman kansu, fararen hula, ilimi da bincike, da abokan hulda, a karkashin kungiyar FAO.

A kasar Senegal, noma na kasancewa har yanzu wani bangaren dake samar da mafi yawan guraben aikin yi. Kana yana wakiltar kashi 70 cikin 100 na al'ummar dake noma, tare da samar da damammaki ta fuskar samar da ayyukan yi, a lokacin da matasa dubu 269 a kowace shekara suke shiga kasuwar aiki, inda kimanin kashi 57 cikin 100 suka fito daga yankunan karkara, in ji Vincent Martin, wakilin FAO a Senegal.

Jami'in ya tabbatar da cewa muradi na uku, wato rage talauci a yankunan karkara na FAO na maida hankali wajen bunkasa samar da damammaki ayyukan karkara masu kyau ga matasan karkara.

Haka kuma wannan aiki, a cewarsa, na bayyana muhimmancin da kungiyar FOA take bayar ga ci gaban matasa a matsayin wani ginshikin rage talauci da kuma kyautata tsaron abinci.

A nasa bangare, Amadou Lamine Dieng, darekta-janar na cibiyar bunkasa samar da ayyukan yi ga matasa ta kasa (ANPEJ), ya nuna cewa noma na zama a halin yanzu a matsayin wani muhimmin makami dake tasiri sosai wajen samar da ayyukan karkara masu kyau ga matasa da mata. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China