in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Zuma ya soki kasashen yamma game da zargin Sin da aikata mulkin mallaka
2015-12-07 09:36:48 cri
Shugaba Jacob Zuma na Afirka ta Kudu, ya soki kasashen yamma bisa zargin da suke yiwa kasar Sin na aikata mulkin mallaka a nahiyar Afirka. Zuma ya ce ko shakka babu Sin na taimakawa Afirka a fannin wanzar da ci gaba.

Shugaban na Afirka ta kudu ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua, kwana guda bayan kammala taron koli na dandalin FOCAC wanda ya gudana a birnin Johannesburg.

A yayin taron da ya gabata, shugaba Xi Jinping ya gabatar da shawarwari 10, game da tsarin da za a bi domin bunkasa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. An kuma fidda sanarwar bayan taro mai kunshe da tsarin inganta hadin kan sassan biyu.

Da yake tsokaci game da hakan, shugaba Zuma ya ce shawarwarin da shugaba Xi ya gabatar sun shaida lura da Sin ke yi ga bukatun Afirka, maimakon zuwa da ra'ayin kashin kai.

Ya ce babu kanshin gaskiya game da rade-radin da kasashen yamma ke yadawa, cewa Sin na gudanar da mulkin mallaka a Afirka, kwatankwacin wanda 'yan mulkin mallaka suka yi a baya, na wawashe albarkatun nahiyar ta Afirka. A cewar sa wasu daga kasashen yamma sun arzuta kan su daga albarkarun nahiyar, ba tare da baiwa Afirka wani tallafi ba. A daya hannun kuwa, Sin na aiwatar da hadin gwiwa da Afirka a dukkanin fannonin ci gaba da suka hada da na siyasa da tattalin arziki da dai sauran su.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China