in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Amurka sun yi tattaunawa karo na farko kan yaki da laifuffukan da aka aikata a kan internet
2015-12-02 11:04:50 cri
An gudanar da taron tattaunawa karo na farko kan yaki da laifuffukan da aka aikata a kan internet a tsakanin Sin da Amurka a birnin Washington a ranar 1 ga wata, inda memban majalisar gudanarwar kasar Sin Guo Shengkun, sakataren harkokin shari'a na kasar Amurka Loretta Lynch da sakataren harkokin tsaron yankunan kasar Amurka Jeh Charles Johnson suka shugabanci taron.

Guo Shengkun ya bayyana cewa, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyara a kasar Amurka a watan Satumba cikin nasara, shugabannin kasashen biyu sun cimma daidaito kan batun tabbatar da tsaron internet, kuma sun tsaida kudurin kafa tsarin tattaunawa kan yaki da laifuffukan da aka aikata a kan internet.

Lynch da Johnson sun bayyana cewa, a matsayin manyan kasashen tattalin arziki a duniya, Amurka da Sin suna da moriya iri daya a fannin tsaron internet. Amurka tana son daukar matakan da shugabannin kasashen biyu suka cimma cikin sahihanci.

A gun taron tattaunawar, bangarorin biyu sun cimma ka'idojin yaki da laifuffukan da aka aikata a internet da sauran batutuwan da abin ya shafa, sun tsaida kudurin kafa tsarin layin musamman na tarho, da cimma daidaito kan warware matsalolin dake shafar tsaron internet, hadin gwiwar yaki da ta'addanci a internet, horar da kwararru a wannan fanni da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China