in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Afirka za su yi bikin baje koli na na'urori a Afirka
2015-11-26 20:09:22 cri
Mataimakin ministan kasuwancin na Sin Qian Keming ya bayyana a yau Alhamis cewa, ma'aikatar kasuwanci ta kasar Sin za ta kira taron shugabannin kamfanonin Sin da Afirka, da kuma bikin baje kolin na'unonin kasar Sin a yayin taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da za a gudanar a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu a watan Disamba na shekarar bana.

Wannan shi ne karo na farko da kasashen Sin da Afirka za su shirya bikin baje koli na na'urori a Afirka tare.

Haka kuma, a yayin taron maneman labaran da aka yi a wannan rana, Qian Keming ya ce, wannan shi ne karo na farko da za a nuna manyan na'urorin da kasar Sin ta ke kerawa a nahiyar Afirka, wannan ya sa kasar Sin ta zabi wasu kamfanonin da suka shahara a fannonin da suka shafi layin dogo, jiragen sama, wutar lantarki, sadarwa da dai sauransu da su halarci bikin.

A halin yanzu kuma, kasar Sin na dukufa wajen inganta hadin gwiwar kasa da kasa game da gina kayayyakin more rayuwa da kuma ciyar da aikin masana'antu gaba, kuma yanzu haka kasashen Afirka na kokarin raya harkokin masana'antu, lamarin da ya sa burin neman bunkasuwa na Sin da Afirka ke dacewa da juna sosai. Don haka ana ganin cewa, hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin biyu na da makoma mai haske. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China