in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi alkawarin tallafawa ci gaban Afirka
2015-11-25 19:08:23 cri
Kasar Sin za ta bayyana wasu shirye-shiryen da ta tanada da nufin taimakawa ci gaban nahiyar Afirka, yayin taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC da zai gudana a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Zhang Ming ya shaidawa taron manema labarai cewa, wadannan tanade-tanade za su taimaka wajen raya masana'antu da bangaren aikin gona na nahiyar.

Shi ma mataimakin ministan kasuwanci na kasar Sin Qian Keming ya bayyana cewa, za a yi baje kolin kayayyakin masana'natu a yayin taron dandalin, bikin da ake fatan zai ba da damar kulla harkokin kasuwanci a bangarorin jiragen kasa da na sama, wutar lantarki da harkokin sadarwa.

Ana kuma sa ran shugabannin siyasa da na masana'ntu za su yi amfani da wannan dama wajen yin musayar ra'ayoyi.

Kimanin shugabannin kasashe 36 da na gwammatoci 5 da mataimakan firaministoci 3 da shugaban hukumar zartaswar kungiyar tarayyar Afirka ne za su halarci wannan taro mai tarihi, inda kasashe masu tasowa za su hadin kan da ke tsakaninsu. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China