in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu ta shirya tsab domin karbar bakuncin taron shugabannin FOCAC
2015-11-26 10:34:49 cri

Kwamitin ministoci a Afrika ta Kudu ya fada a ranar Larabar nan cewar, kasar ta shirya tsab domin karbar bakuncin taron shugabannin dandalin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afrika wato FOCAC.

Kwamitin ya ce, tuni an kammala kimtsawa wajen tanade tanaden kayayyakin da ake bukata yayin gudanar da taron, sannan dukkannin tsare tsare da suka hada da na taron manyan jami'ai, da taron ministoci da sauran muhimman al'amurra da suka shafi taron sun kammala.

Kwamitin ya tabbatar da cewar, an kammala shirya wuraren taro a Pretoria da Johannesburg.

Wannan shi ne karon farko da aka daga likafar taron na FOCAC zuwa matsayin taron shugabanni, wanda za'a gudanar tsakanin ranakun 4 zuwa 5 ga watan Disamba. Ana sa ran shugaba Xi Jinping na kasar Sin, da shugabannin kasashen Afrika da wakilan gwamnatoci za su halarci taron.

Kuma ana sa ran a yayin taron, za'a daddale wani daftari wanda zai tabbatar da hadin kai tsakanin sassan biyu.(Ahmed Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China