in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Turkiya ta harbo jirgin saman yakin Rasha
2015-11-24 19:49:23 cri
Rahotanni daga kasar Turkiya na cewa, dakarunta sun harbo wani jirgin saman yakin kasar Rasha a kusa da kan iyakar Syria da Turkiya.

Wani kamfanin dillancin labarai mai zaman kansa ya ba da rahoton cewa, jirgin ya fado ne a tsaunukan Turkmen da ke yankin Kizidag a kudancin kasar Turkiya.

Gidan talabijin na al-Mayadeen da ke watsa shirye-shiryen cikin harshen Larabci a kasar Syria, ya ruwaito majiyoyin sojan kasar Turkiya na cewa, jirgin saman kasar Turkiya samfurin F-16s ne ya harbo jirgin Rasha, bayan ya yi masa gargadin cewa ya keta sararin samaniyar kasar.

A ranar Jumma'a ne dai ma'aikatar harkokin wajen Turkiya ta kira jakadan kasar Rasha da ke Ankara domin ta bayyana rashin jin dadinta kan hare-haren da Rashar ke kaddamarwa a kauyukan Turkmen da ke arewacin kasar Syria.

Gwamnatin Turkiya dai ta sha yi wa Rasha gargadi kan ta kawo karshen hare-haren da ta ke kaiwa a yankin. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China