in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan ta'adda ne suka kitsa hadarin jirgin kasar Rasha inji FSB
2015-11-17 19:09:54 cri
Hukumar tsaron kasar Rasha ko FSB a takaice, ta ce 'yan ta'adda ne suka haddasa hadarin jirgin fasinjan nan na kasar ya Rasha, wanda ya fadi a ranar 31 ga watan da ya shude a yankin Sinai dake kasar Masar. Duba da hakan, hukumar ta FSB ta ce ana iya ayyana wannan lamari a matsayin aikin ta'addanci.

Da yake karin haske game da ikirarin hukumar ta tsaro, shugaban ta Alexander Bortnikov, ya shaidawa taron manyan jami'an kasar wanda shugaba Vladimir Putin ya jagoranta, cewa kwararru sun tabbatar da wani bam mai karfin gaske ne ya fashe a cikin jirgin, wanda hakan ne kuma ya sanya jirgin tarwatsewa.

Bisa wannan sakamako, shugaban kasar ta Rasha Vladimir Putin, ya umarci sassan hukumomin tsaron kasar sa, da su gaggauta damke dukkanin wadanda ke da hannu a aikata wannan ta'asa a duk inda suke a fadin duniya.

Tuni dai FSB ta bayyana tukwicin dalar Amurka miliyan 50, ga duk wanda ya bada muhimman bayanai da za su taimaka, wajen cafke masu hannu cikin kitsa faduwar jirgin fasinjar kasar ta Rasha.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China