in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya halarci bikin samar da sanarwar shugabanni kan yarjejeniyar RCEP
2015-11-22 17:49:26 cri
Yau Lahadi 22 ga wata, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya halarci bikin samar da sanarwar shugabanni kan cikakkiyar yarjejeniyar tarayyar tattalin arzikin yankin, wato RCEP da aka yi a cibiyar taron kasa da kasa dake birnin Kuala Lumpur na kasar Malaisiya. Shugabannin kasashen kungiyar tarayyar kasashen kudu maso gabashin Asiya ta ASEAN da kuma shugabannin kasashen Koriya ta Kudu, Japan, Australia, New Zealand da Indiya sun halarci bikin, inda shugaban kasar Malaisiya Najib Tun Razak ya gabatar da sanarwar din.

Cikin sanarwar, an ce, shugabannin kasashen da yarjejeniyar RCEP ta shafa suna maraba da sakamakon da aka samu bisa shawarwarin da aka yi, kuma yarjejeniyar na da muhimmiyar ma'ana wajen kyautata zaman rayuwar al'ummomin yankin da kuma raya tattalin arziki, ita ce wata babbar hanya wajen dunkulewar tattalin arziki a wannan yanki. Haka kuma, za ta taimaka ga ciyar da bunkasuwar tattalin arziki cikin adalci, yayin da ake karfafa huldar tattalin arziki a tsakanin kasa da kasa.

Bugu da kari, shguabannin kasashen sun bayyana niyyar sa kaimi wajen karfafa shawarwarin dake tsakanin bangarorin daban daban da abin ya shafa, domin kawo karshensa a shekarar 2016. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China