A cikin kwanaki 3 masu zuwa, firaministan Sin zai halarci taron koli karo na 18 na kasar Sin da kasashen kudu maso gabashin Asiya Asean da taron koli karo na 18 na kasashen Sin, Japan da Koriya ta Kudu da kungiyar Asean da kuma taron kolin kasashen dake yankin Gabashin Asiya karo na 10. Sannan kuma, zai kai ziyara a hukunce a kasar Malaysia. Masana sun nuna cewa, a lokacin da ake samun hadin gwiwar yankin gabashin Asiya, ziyarar firaministan Sin na wannan karo zai kawo kuzari ga aikin dunkulewar kasashen da ke yankin gabashin Asiya baki daya, gami da raya hadin gwiwar dake yankin.(Bako)