in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Mali ta kaddamar da dokar ta baci
2015-11-21 13:24:41 cri
Gwamantin kasar Mali ta kafa dokar ta baci na tsawon kwanaki 10 a yammacin ranar Jumma'an nan bayan da aka hallaka mutane 27 a wani harin ta'addanci da aka kai wani otel a babban birnin kasar na Bamako.

Haka kuma gwamantin ta tsayar da kwanaki uku a matsayin na makoki ga wadanda suka rasa rayukansu da suka hada da Sinawa guda 3, Ba'amurke 1 da da Balgian 1.

Jami'an tsaro na kasar sun kaddamar da ayyukan ceto domin su kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su a wannan otel din guda 170, yawancinsu 'yan kasashen waje na tsawon awanni 9.

A kalla mutane 27 aka tabbatar da mutuwarsu, sannan an riga an kubutar da saura a cikin otel din na Radison Blu kamar yadda ministan tsaro na kasar Salif Traore ya tabbatar, sa'o'i kadan bayan wannan danyen aikin ta'addanci.

'Yan kasar Sin guda 3 an kashe su ne a gwagwarmayar da aka yi da wadanda aka yi garkuwa da su, kamar yadda ofishin jakadancin kasar Sin dake Mali ya tabbatar ma Xinhua a ranar Jumma'a sannan an kubutar da guda 4. (Fataimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China