in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afirka za su iya yin koyi da ci gaban da kasar Sin ta samu, in ji kwararru
2015-11-20 09:26:48 cri
Wani tsohon ma'aikacin bankin duniya kana kwararren mai bincike mai zaman kansa Luke Jordan ya bayyana cewa, ya kamata kasashen Afirka su koyi dabarun da kasar Sin ta yi amfani da su wadanda har suka sanya ta zama kasa ta biyu mafi karfin tattalin arzikin duniya a halin yanzu.

Luke Jordan wanda ya bayyana hakan yayin da ya ke yiwa manema labarai bayani game da dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC a takaice da za a gudanar a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu. Ya ce, kamata ya yi kasashen na Afirka su kara fadada tunaninsu, maimakon dogara kan tallafin kudaden da kasar Sin take ba su.

Ya bayyana cewa, kamata ya yi kasashen na Afirka su yi koyi da dabarun da kasar Sin ta yi amfani da su wajen raya yankunan karkara da zuba makuden kudade a bangaren bincike a manyan makarantu da kuma kafa cibiyoyin nazari.

Shi ma wani babban jami'in bincike a cibiyar nazarin harkokin kasa da kasa ta kasar Afirka ta kudu Romain Dittgen ya bayyana cewa, kasar Sin a shirya ta ke ta yi musayar fasahohinta da kasashen Afirka.

Jami'in ya ce, ana fatan wasu sabbin abubuwa game da dangantakar Sin da Afitka za su bullo, bayan taron kolin na FOCAC da za a yi a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu a watan Disamban wannan shekara.

Ya kuma yaba gudummawar dakarun da kasar Sin ta baiwa MDD wadanda a halin yanzu ke aikin wanzar da zaman lafiya a Afirka (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China