in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin ya yi fatan Sin da Afirka za su karfafa hadin gwiwa karkashin dandalin FOCAC
2015-11-12 09:41:03 cri
Jakadan kasar Sin a kasar Zambia Yang Youming, ya yi fatan ganin an bunkasa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka, karkashin taron dandalin FOCAC, wanda za a gudanar cikin watan Disamba mai zuwa a Afirka ta Kudu.

Mr. Yang, ya ce akwai bukatar sassan biyu su kara azama wajen cin gajiya daga wannan dandali, su kuma fadada alakar su karkashin inuwar manufar hadin kai tsakanin kasashe masu tasowa.

Jakadan na Sin wanda ya yi wannan tsokaci cikin wani sharhi da aka wallafa a jaridar Zambia Daily Mail, ya kara da cewa taron dandalin FOCAC na da dadadden tarihi, zai kuma zamo ginshikin habaka huldar sassan biyu. Kaza lika a cewar sa manufar hadin gwiwa ta tsakanin kasashe masu tasowa da Sin ke aiwatarwa, na kan sahun gaba wajen inganta huldar diflomasiyyar Sin da Afirka, a yunkurin ta na cimma kyakkyawar alaka da sauran kasashen duniya.

Sharhin ya kuma bayyana cewa mafiya yawan kasashe masu tasowa na nahiyar Afirka, kuma nahiyar tana da albarkatu, da ma'adanai masu tarin yawa, baya ga kasuwa da damammaki na samun bunkasa. Don haka ne ma kasar Sin ke fatan tallafawa nahiyar Afirka, a fagen cimma nasarar bunkasar tattalin arziki, da dogaro da kai, tare da samun ci gaba mai dorewa.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China