in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gidan nune-nunen wayin kan bakaken fata 'yan Afrika da Sin ta gina na da ma'anar musamman, in ji ministan al'adu na Senegal
2015-04-24 11:06:03 cri
Ministan al'adu da yada labaru na kasar Senegal Mbagnic Ndiaye ya bayyana cewa gidan nune-nunen wayewin kan bakaken fata da gwamnatin Sin ta ke ginawa, zai zama cibiyar al'adu ga bakaken fata na nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Ministan Ndiaye ya fadi hakan ne, a jiya Alhamis yayin da yake duba aikin gina gidan nune-nunen da gwamnatin Sin ke ginawa

Gidan yana cikin birnin Dakar hedkwatar kasar Senegal, kuma yana kusa da babban dakin wasan kwaikwayon kasar da Sin ta taimaka wajen ginawa. A watan Disamba na shekarar 2013 ne, aka fara aikin gina wannan daki, kuma an kimanta cewa, za a kammala aikin gine-gine don fara amfani da shi wajen nune-nunen kayayyakin fasahohi na bakaken fata a watan Afrila na shekarar 2016.

Bayan da wakiliyar kungiyar UNESCO a yankin yammacin Afrika Saidou Sireh Jallow Ann Therese Ndong-Jatta ta ziyarci wurin, ta ce, gidan nune-nune da Sin ta gina ya cimma burin al'ummar Senegal zuriya bayan zuriya, kuma ya samar da wani dandali wajen nuna wayewar kan bakaken fata a duniya, lamarin da ke da ma'anar musamman wajen sa kaimi ga musayar al'adu da yada akidar zaman lafiya da samun bunkasuwa a duniya.

Jakadan Sin a Senegal Xia Huang ya ce, yayin da firaministan Sin Li Keqiang ya ziyarci Afrika a bara, ya ce, ya zama dole a raya tattalin arziki da cinikayya, da al'adu bai daya, don bunkasa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen Sin da Afrika yadda ya kamata, dakin wasan kwaikwayo da gidan nune-nunen wayewin kan bakaken fata sun kasance muhimman nasarorin da aka samu ta hanyar hadin gwiwar al'adu a tsakanin kasashen biyu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China