in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta nuna damuwa kan halin da yaran ke ciki a Sudan
2015-11-17 09:37:51 cri
Asusun kula da kananan yara na MDD ko UNICEF a takaice ya bayyana matukar damuwa game da mawuyacin halin da kananan yara ke ciki a kasar Sudan.

Alkaluman baya-bayan da asusun na UNICEF ya fitar ya nuna yadda ake samun karuwar mutuwar kananan yara a kasar a watanni biyar na farkon rayuwarsu sakamakon karancin abinci mai gina jiki, inda yara 68 cikin 1,000 ke mutuwa

Mataimakin babban darektan asusun na UNICEF Omar Abdi wanda ya bayyana hakan, bayan ziyarar da ya kai kasar ta Sudan a ranar Lahadi ya ce, yaran na mutuwa ne sakamakon rashin koshin lafiyar mahaifiya da karancin abinci mai gina jiki da kuma matsalolin da matan ke fuskanta a lokacin haihuwa.

Darektan ya ce, hanya guda ta magance cututtukan da ke halaka kaso 6 cikin 100 na yaran ita ce, alluran rigakafi da tsaftace muhalli.

Asusun na UNICEF ya bayyana shirye-shiryen da zai gudanar tare da hadin gwiwar ma'aikatar lafiya ta Sudan don rage yawan yaran da ke mutuwa a kasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China