in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijar: An soke bukukuwan ranar kwadago
2015-05-02 16:25:38 cri
Gamayyar kungiyoyin 'yan kwadago a Nijar sun soke gudanar da bukukuwan da aka saba yi ran 1 ga watan Mayun kowace shekara, domin zagayowar ranar kwadago ta duniya, inda maimakon hakan aka shirya gudanar da addu'o'i na musamman, ga al'ummar kasar da suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren mayakan Boko Haram.

Wata sanarwar da kungiyar 'yan kwadagon kasar ta fitar ta ce 'ya'yan kungiyar sun kadu matuka, bisa kisan bayin Allah a yankin Karamga dake gabashin kasar, lamarin da ake dangantawa da mayakan Boko Haram.

Da yake karin haske game da wannan al'amari, ministan ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar Hassoumi Massaoudou, ya ce yayin harin da mayakan kungiyar suka kaddamar a karshen makon jiya, sun hallaka sojoji 46, da wasu fararen hula 28, kana wasu mutane 9 sun jikkata, yayin da kuma ake ci gaba da neman wasu 32 da suka bace.

Tuni dai mahukuntan kasar suka shelanta fara zaman makoki na kwanaki 3 tun daga ranar 29 ga watan Afrilun da ya shude, domin nuna alhinin kisan 'yan kasar.

A baya dai ana gudanar da bukukuwan ranar kwadago a kasar ta Nijar, kamar yadda hakan ke gudana a sassan duniya daban daban. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China