A yau ne shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya rantsar da majalisar ministocinsa, watanni shida tun bayan da ya kama aiki a watan Mayun wannan shekara.
A jawabinsa yayin bikin rantsar da sabbin ministocin da ya gudana a fadar shugaban kasar da ke Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya, shugaba Buhari ya ce, yana da tabbacin a kansu don haka ya bukace su da su zage damtse don ciyar da kasar gaba.
Shugaba Buhari ya zauna da ministocin a karon farko, jim kadan bayan ya sanar da ma'aikatun da za su rike. Koda ya ke kamar yadda ya nanata tun farko, shi ne zai shugabancin ma'aikatar man fetur ta kasar, bayan da ya nada Ibe Kachikwu a matsayin manajan darektan kamfanin man fetur na kasar.
A jiya ne dai Shugaba Buhari ya sallami manyan sakatarorin kasar guda 17, a wani mataki na yin garambawul ga ayyukan gwamnati. Kuma nan take ya maye gurbinsu da wasu 18.(Ibrahim)