in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: An bude baje kolin kasa da kasa a Lagos
2015-11-08 13:17:08 cri
Wani bakin baje kolin kasa da kasa ya bude a ranar Jumma'a a birnin Lagos na Najeriya, bisa manufar ingiza sabon karfi ga wani tattalin arzikin kasar dake dogaro kawai ga fitar da man fetur, a cewar masu shirya baje kolin.

Fiye da mahalarta dubu 300 da suka fito daga dukkan fadin duniya suka isa wannan babbar haduwa ta shekara, da za ta ci gaba da gudana har zuwa ranar 15 ga watan Nuwamba. Wani adadin 'yan kasuwa dake gudanar da harkoki ta intanet na tsakanin kasa da kasa, sun halarci wannan baje kolin a karon farko, inda suke gabatar da ayyukansu na kasuwanci, haka kuma tare da zummar neman fadada harkokin kasuwanci a birnin Lagos na wannan kasa. He Xiyang, wani mai gabatar da kayayyaki, kuma darektan Steelite Nigeria Limited, wani kamfanin dake hedkwata a jihar Ogun dake kudu maso yammacin Najeriya, ya bayyana cewa wannan baje koli wata babbar dama ce ga kamfaninsa na gabatar da sabbin kayayyakin da ya kera. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China