in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Najeriya ta yi kira ga masu zuba jari da su karkata ga bangaren sadarwa na zamani
2015-10-23 09:47:35 cri
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi kira ga masu sha'awar zuba jari na gida da ketare da su zuba jari a bangaren sadarwa na zamani.

Babban darektan hukumar raya harkokin sadarwa na zamani na Najeriya(NITDA) Peter Jack wanda ya yi wannan kiran a birnin Legas, cibiyar kasuwancin Najeriya. Ya bayyana cewa, zuba jari a wannan sashe zai taimaka wajen bunkasa kasa, baya ga ribar da za a girba nan da nan kan jarin da aka zuba.

Peter Jack ya yi kira ga masu zuba jari daga ketare da su hanzarta cin gajiyar damammakin harkar zuba jari a bangaren sadarwa na zamani a Najeriya. Ya kuma shaidawa manema labarai cewa, a wannan shekara hukumarsa ta shigo da wasu cibiyoyin sadarwa na zamani guda 14 cikin kasar baya ga wasu fitattun kamfanoni da ke cikin kasar da suka baje kolin hidimomin da suke bayarwa ga duniya.

Sashen sadarwa na zamani dai ya taimaka wajen ninka alkaluman GDP na kasar a cikin shekaru biyar din da suka gabata daga kashi 4.5 cikin 100 zuwa kashi 10 cikin 100. Akwai kuma alamun da ke nuna cewa, sashen zai kara bayar da gudummawa ga tattalin arzikin kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China