in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zaunanen wakilin kasar Sin dake MDD ya bayyana matsayin kasarsa kan batun Syria
2015-11-11 14:18:49 cri
A jiya Talata, zaunanen wakilin kasar Sin dake kungiyar MDD mista Liu Jieyi ya bayyana matsayin da kasar sa ta dauka kan batun kasar Syria bayan kwamitin sulhu ya duba yunkurin siyasar kasar.

A cikin jawabin da ya yi a gaban manema labaru, Liu ya bayyana cewa, kasar Sin ta yi maraba da fadaden taron ministocin harkokin waje na kasashen dake shafar batun Syria da aka shirya a kwanan baya a Viena.

Liu ya kara da cewa, kwamitin sulhu ya riga ya zartas da kudurori da dama kan batun yaki da kungyiyoin 'yan ta'adda, ciki har da IS, an kuma samu ra'ayi bai daya a kai. Kasashe mambobin kwamitin, ciki har da Sin, da kuma kasashe masu halartar taron ministan harkokin waje na Viena dukkansu na goyon bayan yaki da kungiyar IS da sauran 'yan ta'adda bisa kudurin kwamitin sulhu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China