in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci a warware batun Syria ta hanyar siyasa
2014-06-05 20:16:30 cri
Kasar Sin ta yi kira ga dukkan sassan da batun Syria ya shafa da su rungumi hanyar siyasa wajen warware rikicin kasar, bayan da shugaban kasar mai ci Bashar al-Assad ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya fada yayin taron manema labarai cewa, hanya daya tilo ta magance rikicin kasar komai muninsa, ita ce hanyar siyasa.

Hong ya ce, kamata ya yi gwamnatin Syria, jam'iyyun adawa da sauran masu ruwa da tsaki, da su sanya muradun kasar da jama'arta a gaban komai kana su kawo karshen fada da tashin hankalin da ke faruwa a kasar, su kuma mayar da hankali kan tattaunawar Geneva.

A ranar Laraba ne majalisar dokokin kasar ta Syria ta bayar da sanarwar cewa, shugaba al-Assad ya lashe kashi 88.7 cikin 100 na kuri'un da aka kada, lamarin da ya ba shi damar ci gaba da wa'adi na uku na tsawon shekaru 7 yana mulki.

Wannan shi ne karo na farko a tarihin kasar Syria da aka gudanar da zaben shugaban kasa da 'yan takara da dama, matakin da 'yan adawa da ke ketare da kasashen yammaci da ke mara musu baya suka yi watsi da shi. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China