in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan taron Vienna zai samar da mafita a siyasar Syria
2015-10-30 20:49:48 cri
Kasar Sin ta bayyana goyon bayan ta na son ganin an samu ingantacciyar mafita lokacin taron Vienna akan kasar Syria, kamar yadda kakakin ma'aikatar harkokin wajen ta Lu Kang ya bayyana a yau jumma'a lokacin taron manema labarai.

A ranar alhamis ne dai manyan jami'ai daga Amurka,Rasha,Saudia da Turkiya suka hadu a tattaunawa karo na farko a Vienna don tatauna yadda za'a warware matsalar da Syrian ke fuskanta.

Mataimakin Ministan harkokin wajen kasar Sin Li Baodong ya halarci zaman tattaunawar na musamman da aka kira na yau jumma'an a Vienna wanda ya hada dukkannin jami'an diflomasiya daga kasashen da dama da suka hada da Iran.

Kasar Sin dai ta dade tana maida hankalin ta a yanayin siyasar da kasar Syria ta tsinci kanta a ciki inda take bada goyon bayan tattaunawa kamar yadda sauran kasashen duniya suke yi, inji Kakakin Lu Kang.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China