in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An cafke mutum na biyu da sojojin Najeriya ke nema ruwa a jallo
2015-11-11 09:56:42 cri
Rundunar sojin Najeriya ta ce ta samu nasarar cafke mutum na biyu, da take zargi da hannu cikin kitsa hare-haren da kungiyar Boko Haram ke kaddamarwa.

Wata sanarwar da rundunar ta fitar ta ce wanda aka cafke mai suna Ishaku Wardifen, daya ne daga mutane 100 da ta dade tana nema. Ya kuma shiga hannu ne a ranar Litinin, a kauyen Maliha dake jihar Adamawa. Sanarwar ta kuma ce binciken farko da rundunar ta gudanar ya nuna cewa Wardifen dan asalin kasar Kamaru ne.

A ranar Lahadin karshen mako ne jami'an rundunar suka kame Chindo Bello, wanda shi ne na farko da ya shiga hannu, tun bayan fidda sunayen wadanda ake zargin makwanni 3 da suka gabata. An cafke Bello ne a filin sauka da tashin jiragen sama na Nnamdi Azikwe dake birnin Abuja, a kan hanyar sa ta zuwa birnin jihar Legas. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China