in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya lashi takwabin hanzarta zurfafa gyare-gyaren tattalin arziki
2015-11-10 18:45:53 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Sin za ta hanzarta gudanar da gyare-gyare a fannin tattalin arziki a matsayin ginshikin karfafa samun dauwamammen ci gaba.

Shugaba Xi wanda ya bayyana hakan yayin taron kungiyar kula da harkokin kudi da tattalin arziki ta kwamitin tsakiya na JKS, ya ce, za a yi amfani da manufofi da nagartattun tsare-tsaren harkokin kudi yayin da ake kokarin samar da yanayin gyare-gyaren tattalin arzikin da ya dace a cikin gida.

Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, kamata ya yi gwamnati ta bullo da manufofin da suka dace ga harkokin masana'antu ta yadda za su tallafawa tsarin tattalin arzikin kasar tare da inganta yanayin kasuwannin da za su taka muhimmiyar rawa a bangaren masu sayen kayayyaki.

Bugu da kari, shugaban ya ce kamata ya yi gwamnati ta mayar da hankali wajen rage matsalar yawan kayayakin da masana'antu ke samarwa, da rage kudaden tafiyar da kamfanoni da cunkuson kasuwannin sayar da gidaje tare da gina kasuwar hada-hadar kudi mai inganci da kuma kare 'yancin masu zuba jari. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China