in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya ta rasa damar karbar bakuncin gasar kwallon raga, a yanzu Congo Brazzaville ce zata karbi bakuncin
2015-11-10 15:17:03 cri
Kasar Kenya ta rasa damar ta na karbar bakuncin wasan share fagen cin kofin Olympic na Afrika ta fuskar wasan kwallon raga wanda ake sa ran gudanarwa a birnin Nairobi a watan Janairun shekarar badi, a halin yanzu, hukumar shirya wasan kwallon raga ta Afrika CAVB, ta zabi Congo Brazzaville a matsayin wacce zata karbi bakuncin gasar.

A wata sanarwar da CAVB ta fitar a Litinin din nan, ta ce Congo Brazzaville za ta karbin bakuncin wasan da ake sa ran gudanarwa tsakanin ranakun 7 zuwa 14 ga watan Janairun shekara mai zuwa.

Brazzaville, ta taba karbar bakuncin gasar wasanni ta Africa a watan Satumba, a don haka CAVB ta ce ta gamsu da ingancin kayayyakin aikin da kasar ke da su na karbar bakuncin gasar wasannin.

Dama dai CAVB ta ayyana cewar, za ta zabi kasa guda ne daga Afrika don karbi bakuncin wasannin, kuma kungiyar wasan raga ta kasar Kenya ta sha zawarcin karbar bakuncin wasan, amma daga bisani Brazzaville ta yi nasarar karbar bakuncin gasar.

Kasashen da suka yi rajistar fafatawa a gasar sun hada da Algeria, da Tunisia, da Gambia, da Cape Verde, da Mali, da Burkina Faso, da Najeriya.

Sauran su ne Ghana, da Central Africa, da Congo Brazzaville, da Congo RDC, da Cameroon, da Gabon, da Kenya, da Masar, da Sudan, da Uganda, da Angola, da Mozambique, da Zimbabwe, da Botswana, da kuma Madagascar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China