in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Super Eagles ta Najeriya na shirin tunkarar ragowar wasannin ta na neman gurbi a gasar cin kofin duniya na 2018
2015-11-10 10:43:11 cri
Kungiyar kwallon kafa ta Najeriya wato Super Eagles, za ta fara atisaye a yau Talata, gabanin buga wasannin ta na share fagen gasar cin kofin duniya na shekarar 2018.

'Yan kwallon Super Eagles din za su fara atisayen ne kafin wasan su na farko, cikin zango na biyu na wasannin fidda gwani wanda za su buga da kasar Swaziland a birnin Lobamba.

A cewar mai magana da yawun kungiyar Toyin Ibitoye, za a fara tara 'yan wasan ne domin samun horo tun da wuri, duba da yadda wasun su ke makara a duk lokacin da ake bukatar su halarci wasa ga kungiyar ta Super Eagles.

Ibitoye ya ce masu tsaron gida ne kadai suka gudanar da atisaye a jiya Litinin, kuma ya zuwa karfe 4 na yammacin jiyan, duka-duka 'yan wasa 8 ne suka halarci sansanin da aka bude ga 'yan wasan. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China