in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso: Faransa ta jaddada wani shirin kan iyaka domin yaki da ta'addanci
2015-11-05 11:06:39 cri
Shugaban rundunar sojojin Faransa, janar Pierre de Villier ya jaddada, a ranar Talata da yamma a birnin Ouagadougou, kan wajabcin bullo da wani shirin kan iyaka domin yaki da barazanar ta'addanci da kasashen dake yankin Sahel suke fuskanta.

Dukkan kasashen dake yankin Sahel matsalar ta'addanci ta shafe su. Dalilin haka ne ya kamata mu yi aiki tare, domin har yanzu akwai 'yan ta'adda a arewacin wannan yanki, har ma da Boko Haram, kuma suna kai hare hare a ko ina a inda suke iya kaiwa. Idan muna kara karfi cikin hadin gwiwa, ba shakka tashin hankali zai ja da baya, in ji janar Pierre de Villiers, bayan gana da shugaban rikon kwarya na Burkina Faso, Michel Kafando. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China