in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An mika jagorar juyin mulki a Burkina fasa ga mahukuntar gwamnatin wucin gadi
2015-10-02 13:06:32 cri
An kame tare da mika Gilbert Diendere jagoran juyin mulkin da aka yi yunkuri a kasar Burkina Faso ga mahukuntar gwamnatin wucin gadi a ranar Alhamis din nan kamar yadda wani jami'i ya tabbatar.

Gilbert Diendere dai tun da farko ya nemi mafaka ne a gidan wakilin Vatican a kasar wanda daga baya aka kama shi bayan da sojojin dake biyayya ga gwamnati suka kai harin da ba na zubar da jini ba a manyan wuraren da sojojin rukunin juyin mulkin suke da karfi, sannan komai ya koma yadda ya kamata bisa kundin tsarin mulki a kasar dake yammacin Afrika.

Birgediya janar Gilbert Diendere dai an ce an mika shi hannun gwamnati domin ya amsa laifinsa.

Jagoran juyin mulkin ya ce damuwar shi kadai shi ne game da tsaron shi da na iyalin shi saboda yunkurin juyin mulkin ya samu suka daga daukan al'ummar kasar tare da kawo tashin hankali har wassu sun rasa rayukan su wadansu kuma kusan 200 suka jikkata.

A cewar majiyar soji fiye da rabin bangaren sojojin fadar shugaban kasar da aka rusa wato RSP, da rukunin sojoji na musamman 1300 da suka yi yunkurin juyin mulkin sun mika wuya kuma har yanzu suna kan mikawa. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China