in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana kan hanyar rushe jam'iyyun siyasa dake da hannu a yunkurin juyin mulki a Burkina Faso
2015-10-08 10:48:58 cri
Jam'iyyun siyasa da ake zarginsu da hannu a yunkurin juyin mulki na ranar 16 ga watan Satumba a Burkina Faso, za su iya fuskantar matakin rushewa,a cewar wata majiyar shari'a ta kasar a ranar Laraba.

Idan wadannan jam'iyyun siyasa, a karkashin hedkwatocinsu aka tabbatar suna da hannu, to hakan zai kai ga tsige su kwata kwata daga fagen siyasa, in ji Rene Bagoro, alkali kuma ministan muhalli na gwamnatin wucin gadi a yayin wani taron manema labarai.

A cewar alkali Rene Bagoro, jam'iyyun siyasa ana daukarsu a matsayin mutane masu dattako, don haka ana iya hukunta wani mutum mai dattako idan ya aikata laifi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China