in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Burkina Faso ta yi alkwarain yin adalci a hukunci 'yan yunkurin juyin mulki
2015-10-03 13:17:53 cri
Gwamnatin kasar Burkina Faso ta bada tabbacin cewa wadanda suka yi yunkurin juyin mulki a watan da ya wuce karkashin jagorancin Janar Gilbert Diendere za'a yi musu hukunci cikin adalci.

A cikin wata sanarwar gwamnati da aka fitar, an tabbatar da cewa, an riga an fara zaman sauraron shari'arsu, sannan kuma ana bincike da tambayoyi har ma da binciken gidajen wadanda ake zargi.

Janar Diendere wanda ya shirya yunkurin juyin mulkin a ranar 17 ga watan Satumba a kan gwamnatin wucin gadi kuma daga baya ya nemi mafaka a gidan ofishin jakadancin Vatican dake kasar a Ouagadougou, an mika shi ga hukumomi domin ya amsa laifin shi.

Tsohon babban hafsan sojin kasar a lokacin mulkin Blaise Campore wanda aka hambarar a watan Oktoban bara ya yi alkawarion mika kanshi ga muhukunta domin amsa laifin shi game da yunkurin juyin mulkin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 11 sannan wadansu 200 suka jikkata. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China