in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojin sama na Rasha sun kaddamar da hari a Syria ne ba don kare gwamnatin shugaba Assad ba
2015-10-02 13:21:42 cri
A ranar Laraban makon nan ne sojojin sama na kasar Rasha suka kaddamar da hari a kasar Syria bayan makonni da suka shafe suna shirin yin hakan a lardin Latakia na Syria dake kan bakin teku,

Ministan harkokin wajen kasar ta Rasah Sergey Lavrov a jiya Alhamis ya kare aniyar kasar na harin bama bamai da take yi a Syrian, yana mai cewa, hakan an yi shi ne a kan 'yan ta'adda ba wai don a ci gaba da mara ma Shugaban kasar Bashar Al-Assad bayan ya ci gaba da mulki ba.

Ya ce suna ganin juna gaba da gaba tsakaninsu da sojojin Amurka da su ma suke harin kungiyar ISIL, Al-Nusra da sauran kungiyoyin 'yan ta'adda a lokacin da yake bayani a cibiyar MDD wanda ya ce suna da aniya iri daya.

A wani bangaren kuma hukumar tsaron Amurka ta Pentagon a ranar Alhamis din ta ce Amurkan da Rasha sun yi tattaunawar farko a game da harin sama da suke aiwatarwa a Syria.

Kakakin Pentagon Peter Cook ya ce tattaunawar na tsawon awa daya an maida hankali ne hanyoyin da za'a bi a aiwatar da harin cikin tsanaki ba tare da hadari ba.

Ya ce Amurka ta fara bayar da shawarari a inganta kai harin cikin tsanaki, a kiyaye lissafi bisa kuskure da kuma kauce ma daukan matakan karfi, ayyuka da tafiyar da duk wani abin da zai kawo zaman fargaba. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China