in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hollande da Merkel sun bukaci shugaba Putin da ya kaddamar da hari a kan IS kadai a Syria
2015-10-03 13:30:45 cri
Shugaban kasar Faransa Francois Hollande da shugabar gwamnatin Jamus Angela Markel, sun bukaci shugaba Vladimir Putin na Rasha da ya tabbatar da cewar hare-haren da yake kaddamarwa ta jirgin sama bai wuce kan kungiyar IS ba.

Shubannin biyu, sun yi wannan kiran ne yayin wani taro a jiya Jumma'a a birnin Paris, inda suka gargadi mista Putin da cewar ya tabbatar harin jiragen saman a Syria bai wuce iya maboyar 'ya'yan kungiyar ta IS ba.

Bayan kammala tattaunawa kan warware rikicin Ukraine da shugabannin suka gudanar, Merkel ta ce yanzu babban abin da ke gabansu shi ne ganin bayan kungiyar ta IS domin a cewarta a bayyane take abokan gaba ne, kuma yin galaba a kansu shi ne zai share fagen warware rikicin kasar Syria.

Da ma dai kafin gudanar da tattaunawa kan makomar Ukraine, shugaba Hollande ya yi wata ganawa da Shugaba Putin, kan yadda za'a tunkari shugaban Syria Bashir al-Assad domin kafa gwamnatin rikon kwarya da nufin warware rikicin siyasa a Syria. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China