in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardar MDD ya soki hari a kan sansanin 'yan gudun hijira na Iran dake Iraki
2015-10-31 12:45:34 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-Moon a ranar Jumma'an nan ya soki harin da aka kai ma sansanin Hurriya na 'yan gudun hijira 'yan kasar Iran dake kasar Iraki dake kusa da filin saukan jiragen sama na kasa da kasa na Bagadaza.

A cikin wata sanarwar da kakakin majalissar ya fitar, wannan harin da ya auku a ranar Alhamis ya shafi har da jami'an tsaro 'yan kasar ta Irakin dake harabar sansanin.

Mr. Ban baya ga kira da ya yi ma gwamnatin Iraki da ta tabbatar da ta binciki wannan lamari tare da gurfanar da masu laifi gaban shari'a ya kuma jaddada cewa babu dalilin kai irin wadannan hare-hare.

Magatakardar ya tunatar da gwamnatin ta Iraki har ila yau cewa nauyi ne da ya rataya a wuyanta na tabbatar da tsaro ga al'ummar dake wannan sansani.

Haka kuma ya jaddada kudurin majalissar na ci gaba da samar da mafita na taimakon jin kai ga wadanda ke zaune a sansanin na Huriyya tare da yin kira ga gwamnatin na Iraki da masu ruwa da tsaki na sauran kasashen duniya da su gaggauta shirin canza sansanin a matsayin wani mataki na kare lafiyar da samar da karko ma mazauna wajen. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China