in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya yi kiran da a sassauta rikicin dake ruruwa tsakanin Isra'ila da Palasdinu
2015-10-17 13:39:45 cri
Kasar Sin ta bukaci bangaren Palasdina da na Isra'ila da su kai zuciya nesa gwargwadon iko, su kuma samar da hanyar da za ta sassauta kara ruruwan rikici a tsakanin su.

Wakilin kasar Sin na din din din a MDD Liu Jieyi ya bayyana hakan a lokacin taron gaggawa na kwamitin tsaron majalissar a kan wutan dake kara ruruwa tsakanin Isra'ila da Plasdinu.

Ya ce rashin jituwa tsakanin bangarorin biyu ya kara ruruwa, abin da ke janyo damuwa game da yanayin tsaro a kudancin Kudus, yammacin kogin da ma Gaza. Abin da in ji wakilin Sin yake saka kasar damuwa matuka.

Liu Jieyi ya ce ya kamata kasashen duniya musamman kwamitin tsaron majalissar su mai da hankali sosai a kan bukatar Palasdinu da na kasashen Larabawa. Ta hanyar inganta kokarin bangarorin da abin ya shafa domin samun su tsagaita bude wuta dake wakana a tsakaninsu kuma rage zaman fargaba da ake fuskanta a yankin.

Wakilin dindindin a MDD har ila yau ya ce cimma nasarar samar da zaman lafiya a tsakanin Palasdinu da Isra'ila shi ne hanya mafi dacewa ta warware takaddamar dake tsakanin bangarorin biyu daga nan sai ya bayyana fatan cewar gwamnatin Isra'ila za ta dauki darasi ta hanyar misali mai kyau da kuma bayyana aniya na gari. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China