in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Palesdinu ta yi tir da ayyukan ta'addanci da Isra'ila ta gudanar
2015-10-30 10:54:34 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Palesdinu ta bayar da sanarwa a jiya Alhamis inda ta yi tir da ayyukan ta'addanci da gwamnatin kasar Isra'ila ta gudanar a kan Palesdinawa.

Sanarwar ta yi nuni da cewa, firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bada shawarar kafa wata kotun shari'ar harkokin jama'a don sa kaimi ga daukar matakan yanke hukunci ga Palesdinawa, kana za ta bayar da umurnin tsarewa, da rushe gidaje da dai sauransu.

Tun a karkon watan nan ne, ake fuskantar zaman dar-dar a tsakanin Palesdinu da Isra'ila. Kididdiga na nuna cewa, kimanin Palesdinawa 60 ne suka mutu a sakamakon rikicin da ya kazanta, kana mutane fiye da 2000 suka ji rauni, baya ga mutane fiye da dari daya da ka kama. A yayin da 'yan Isra'ila 11 suka mutu kana fiye da mutane 100 suka ji rauni.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China