in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta fara wasannin share fagen Olympics a ranar 21 ga watan Nuwamba
2015-10-29 13:28:03 cri

Wani babban jami'i a hukumar wasanni ta Najeriya NSC ya fada a Litinin din nan cewa kungiyar 'yan wasan Najeriya za ta fara wasannin share fagen Olympics na shekarar 2016 a ranar 21 ga watan Nuwamba mai zuwa.

Alhassan Yakmut, darekta janar na hukumar wasanni ta Najeriya, ya sanar da haka ne a yayin zantawarsa da manema labaru a birnin Abuja, fadar mulkin kasar. A cewarsa, tsarin da za a bi wajen share fagen wasannin Olympics zai sha banban da fasahar da aka yi amfani da ita domin share fagen gasar All African Games.

Jami'in ya kara da cewa yanzu an riga an fara kokarin kulla kwantiragi tare da cibiyoyin horas da 'yan wasa daban daban don samar da dakunan wasanni ga 'yan wasan Najeriya ta yadda za su kimtsa sosai domin tunkarar wasannin Olympics da za a gudanar a Brazil a shekarar 2016.

Ban da haka a cewar mista Alhassan, a halin da ake ciki babu bukatar sanya 'yan wasan Najeriya su taru a wani wuri, sai dai za a kebe duk 'yan wasan kasar masu halartar wasannin Olympics cikin wata cibiya ta musammam dake birnin Rio a makwanni 2 kafin fara wasannin na Olympics.

Har ila yau, jami'in ya ce ana kokarin kimtsawa domin gudanar da wasanni raya al'adun gargajiya na kasar wadda aka shirya gudanarwa a bana amma daga bisani aka dage shi zuwa shekara mai zuwa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China