in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
PSG ya fi Bayern, in ji Zidane
2015-10-15 09:35:51 cri
Tsohon dan wasan kwallon kafa na kasar Faransa Zinedine Zidane ya ce idan an kwatanta kulof din kasar Faransa Paris Saint-Germain, wato PSG da Bayern Munich na kasar Jamus, kulof din PSG ya fi haifar da barazana ga Real Madrid, a takararsu domin lashe kofi a gasar zakarun Turai.

Zidane, wanda ke aiki a matsayin babban koci na Castilla, kungiyar matasa ta Real Madrid, ya ce PSG da Real Madrid su ne kuloflika guda biyu da suka fi yiwuwar cin nasara a gasar zakarun Turai ta wannan kakar wasa.

Zidane ya fadi haka ne yayin da yake hira da wata tashar gidan telabijin ta kasar Faransa, inda ya ce 'yan wasan PSG sun san tsarin gasar Faransa sosai, har ma karfinsu ya wuce na dukkan kuloflika kasar Faransa.

Sai dai ko da yake PSG ya lashe kambin gasar Ligue 1 a kakar wasa guda 3 a jere, hakika a duk wadannan shekaru 3 kulof din ya na komawa baya ne a zagayen kusa da na karshe wato "quarterfinal" a Turance, tun bayan da ya koma gasar zakarun Turai a shekarar 2012.

A kakar wasan da muke ciki, PSG ta ci nasara a wasannin 2 da suka gudana tsakanin rukunin A, inda ya lashe Malmo, da Shakhtar Donetsk, amma a zagaye mai zuwa zai kara da Real Madrid cikin wasanni 2.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China