in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Afirka ta kudu za ta takaita sharudan neman izinin ziyartar kasar ga kasashen BRICS
2015-10-25 13:38:40 cri
A ran 23 ga wata, gwamnatin kasar Afirka ta kudu ta shelanta cewa, za ta nazarta kan yadda za a takaita sharudan neman izinin ziyartar kasar ga 'yan kasashen BRICS kamar Sin da Rasha da Indiya, a yayin da take takaita yawan takardun shaida da masu yawon shakatawa na kasashen waje suke gabatar domin yawon bude ido a Afirka ta kudu tare da yaransu, ta yadda za a rage hasarar da aka kawo wa kasar sakamakon kaddamar da sabuwar manufar neman izinin shiga kasar a watan Yunin bana.

Gwamnatin kasar Afirka ta kudu ta bayyana cewa, bayan da aka aiwatar da sabuwar manufar, yawan hasarar da aka samu a wasu wuraren yawon shakatawa kamar a Dutsen Tebur na kasar ya riga ya kai dalar Amurka miliyan 540.

Sakamakon haka, ma'aikatar kula da harkokin cikin gida ta kasar ta tsai da kudurin yin kwaskwarima kan manufar neman izinin shiga kasar bisa matakai 3, wato, a cikin watanni 3 masu zuwa, masu yawon shakatawa na kasashen waje za su iya gabatar da takardun neman izinin shiga kasar Afirka ta kudu ta hanyar aike da takardunsu zuwa ofisoshin jakadancin kasar dake kasashen duniya ta gidajen waya maimakon zuwa da kansu. Sannan a cikin shekara daya mai zuwa, mai yiyuwa ne kasar Afirka ta kudu za ta yarda da masu yawon shakatawa na kasashen BRICS, kamar na Sin da Rasha da Indiya da su ziyarci kasar Afirka ta kudu ba tare da izini ba.

Ma'aikatar kula da harkokin cikin gida ta kasar Afirka ta kudu ta jaddada cewa, wadannan sabbin manufofi za su iya samun daidaito tsakanin batun tsaron kasar da moriyar tattalin arzikin kasar, amma ba za su kawo barazana ga yara ba. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China