Rundunar sojojin Kamaru ta bayyana cewa, wasu dakaru da ake zaton mayakan 'yan kungiyar Boko Haram ne sun kai farmaki garin Kerawa da ke yankin arewa mai nisa na kasar Kamaru, inda suka halaka mutane 9, kana suka yi garkuwa da mutane fiye da 20.
Ban da haka kuma, sojojin kasar Kamaru sun bayyana cewa, an kai farmaki sau 4 a ranar Laraba na wannan mako a yankin.(Lami)