in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin bom ya hallaka mutane 8 a arewacin Kamaru
2015-10-12 10:21:08 cri

Jami'an tsaro sun tabbatar wa kamfanin dillancin labaran kasar Sin Xinhua cewar, a kalla mutane 8 ne suka mutu a ranar Lahadin nan a sakamakon wani harin kunar bakin wake a yankin Sangueleri dake arewacin kasar Kamaru a kusa da iyakar Kamarun da Najeriya.

A cewar majiyar, wata mata 'yar kimanin shekaru 25 ne ta tada bom din dake jikinta da misalin karfe 8 na safe, kuma nan take bom din ya hallaka ta da saura mutane 7, yayin da wasu mutane 6 suka samu raunuka.

Wannan shi ne hari na 14 a jerin hare haren da aka kai a arewacin Kamaru daga farkon watan Yunin wannan shekara.

Ko da yake babu wata kungiya da ta dauki nauyin kai harin, amma jami'an tsaro na zargin kungiyar Boko Haram da ta kai harin.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China