in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta jaddada aniyar kawo karshen rikicin siyasar Libya duk da matsalolin da ake cin karo da su
2015-10-22 09:34:37 cri
Wakili na musamman ga babban sakataren MDD dake kasar Libya Bernardino Leon, ya fada a Larabar nan cewer, za'a cigaba da daukar matakan warware rikicin sisayar Libya ta hanyar tattaunawa, duk da watsin da Libyan ta yi da bukatar da MDD ta gabatar na neman kafa gwamnatin Hadaka a kasar.

Da ya ke zantawa da manema labarai, mataimakin kakakin wakilin na musamman Farhan Haq, ya ce, Mista Leon, ya tabbatar da cewar za'a ci gaba da daukar matakan kafa gwamnatin Hadaka a kasar, duk da irin yunkurin kafar ungulu da ake neman yiwa shirin.

Leon, ya ce galibin al'ummar Libya na bukatar ganin an kawo karshen rikicin kasar, don haka ya zama tilas a cigaba da tuntubar bangarorin da ba sa ga maciji da juna domin warware rikicin da ya dabaibaye kasar, duk da sanarwar da shugaban majaisar dokokin kasar ya bayar na yin fatali da bukatar MDD kan batun magance rikicin kasar.

Libiya ta fada cikin tashin hankali ne, yayin da tsagin gwamnati wanda kasashen duniya ke marawa baya ke takun saka da bangaren zababbiyar majalisar dokokin kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China