in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta tura sojojin kasa zuwa kasar Yemen
2015-10-19 10:52:05 cri
Kakakin sojojin hadin gwiwa na kasa da kasa dake karkashin jagorancin kasar Saudiyya Ahmed ya bayyana a ranar 18 ga watan nan cewa, wata tawagar sojan kasar Sudan ta isa mashigin tekun Aden na kasar Yemen ta hanyar jiragen ruwa a ranar 17 ga watan nan don gudanar da aikin hadin gwiwa na taimakawa gwamnatin Yemen wajen aikin tabbatar da zaman lafiya.

Ahmed ya bayyanawa 'yan jaridu cewa, muhimmin aikin tawagar sojojin Sudan shi ne taimakawa Yemen wajen tabbatar da zaman lafiya da yaki da ta'addanci a karkashin jagorancin sojojin hadin gwiwa.

Kana ya ce, sojojin hadin gwiwa sun bude kofa ga dukkan sojojin kasashen Larabawa don taimakawa gwamnatin Yemen da zummar samun zaman lafiya mai dorewa a kasar.

Bisa labarin da sojojin hadin gwiwa suka bayar, an ce, tawagar sojojin Sudan ta yi sansani ne a manyan unguwannin birni Aden gabannin isowarsu don taimakawa wajen aikin tabbatar da tsaro.

A watan Yuli na bana, sojojin gwamnatin kasar Yemen masu goyon bayan shugaban kasar Abd-Rabbu Mansour Hadi, da dakarun kabilu sun kwace Aden daga hannun dakarun Shiite Houthi da sojojin tsohon shugaban kasar Salih wadanda suka mallaki yawancin yankunan kasar. Daga baya, gwamnatin Yemen ta yi hijira zuwa Aden daga birnin Riyadh na kasar Saudiyya, amma ba a sassauta halin da ake ciki ba a Aden. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China