in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
FAO ta yi kira ga kara bada kariya ga mazauna karkara
2015-10-14 10:58:24 cri
Hukumar samar da abinci da aikin gona ta duniya wato FAO ta gabatar da rahoton shekara-shekara a jiya talata 13 ga wata, inda ta yi kira ga kara bada kariya daga al'umma ga mazauna karkara don warware matsalolin da suke fuskanta.

FAO ta bayyana a cikin rahoto mai taken "yanayin abinci da aikin gona na shekarar 2015" cewa, yawancin kasashen duniya suna da karfi wajen bada kariya ga mazauna karkara ciki har da kasashe mafi talauci. FAO ta yi hasashe cewa, idan aka zuba jari dala biliyan 67 ga aikin gona da mazauna karkara a kowace shekara, za a cimma burin kawar da talauci a shekarar 2030.

Rahoton ya yi nuni da cewa, hanyar bada kariya daga al'umma ga mazauna karkara ba za ta tabbatar da kawar da taulauci da yunwa a dogon lokaci ba, don haka akwai bukatar a hada kai da kuma daidaita jarin da ake zuba daga al'umma ga mazauna karkara da jarin da ake zuba daga gwamnati da masu zaman kansu ga aikin gona, ta yadda za a iya kawar da talauci a kauyuka ta hanyar samun bunkasuwar tattalin arziki mai dorewa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China