in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Iran ta amince da shirin daukar matakai game da batun nukiliyar kasar
2015-10-13 16:07:10 cri
Bisa labarin da gidan talibijin na kasar Iran ya bayar da safiyar yau din nan, a yayin wani taron da aka gudanar, majalisar dokokin kasar ta kada kuri'ar amincewa da "shirin daukar matakai daga dukkan fannoni" game da batun nukiliyar kasar ta Iran.

A ranar 14 ga watan Yulin wannan shekara ne, aka kulla wannan "shiri na daukar matakai daga dukkan fannoni" game da batun nukiliyar kasar a birnin Vienna na kasar Austria a tsakanin kasar Iran da manyan kasashe 6, wato Amurka, Rasha, Faransa, Ingila, Jamus da kasar Sin. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China