in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a aiwatar da yarjejeniyar nukiliyar Iran a dukkan fannoni
2015-09-16 11:21:38 cri

Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wang Min ya bayyana a jiya Talata cewa, yarjejeniyar da aka cimma game da nukiliyar Iran a dukkan fannoni za ta taimaka wajen tabbatar da hana yaduwar makaman nukiliya a duniya, da sa kaimi ga samun zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya, don haka yana fatan bangarori daban daban da batun ya shafa za su aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata.

Wang Min ya bayyana a gun taron kwamitin sulhun MDD kan aikin binciken kwamitin kula da sanyawa Iran takunkumi cewa, aiwatar da yarjejeniyar nukiliyar Iran a dukkan fannoni shi ne matakin farko na warware matsalar nukiliyar kasar ta Iran, don haka aiwatar da yarjejeniyar yana da matukar muhimmanci.

Lu Kang ya bayyana cewa, Sin tana fatan bangarori daban daban za su yi kokari tare don sa kaimi ga kasar Iran ta kara baiwa hukumar IAEA hadin kan da ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China