in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An nazarci shirin shekaru biyar-biyar na 13 na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin
2015-10-12 19:31:54 cri
A yau ne a nan kasar Sin aka kaddamar da taron hukumar siyasa ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin inda aka nazarci wasu muhimman batutuwa, ciki har da shirin shekaru biyar-biyar karo na 13 na bunkasa tattalin arziki da zamantekwar kasar Sin, da "matakan yakar cin hanci da karbar rasha na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin" da "sharudan yanke hukunci kan 'yan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin wadanda suka keta doka da nuna rashin da'a". Mr. Xi Jinping, babban sakataren kwamitin tsakiya na jam'iyyar shi ne ya shugabanci taron.

A yayin taron, an tsai da kudurin kaddamar da cikakken zama karo na biyar na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin na 18 daga ran 26 zuwa 29 ga watan Oktoban a nan birnin Beijing.

Bugu da kari, mambobin hukumar siyasa ta jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin sun saurari rahoto game da ra'ayoyin da jama'a suka gabatar kan shirin shekaru biyar-biyar na 13 na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin, inda suka tsai da kudurin cewa, za a yi wa shirin gyaran fuska bisa ra'ayoyin da jama'a suka gabatar, za kuma a gabatar tare da tattaunawa a kansa a yayin cikakken zama karo na 5 na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin na 18. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China